fidelitybank

Jami’ar Bayero ta sake dawo da karatun share fage tun bayan shekaru 10

Date:

Jami’ar Bayero, da ke Kano (BUK), ta sake farfado da shirin share fagen shiga Jami’a domin taimakawa daliban da basu samu damar shiga karatun digiri kai tsaye ba.

A tuna cewa an dakatar da shirin shekaru fiye da goma da suka wuce.

Sanarwar ta fito daga bakin Shugaban jami’ar Bayero, Farfesa Sagir Adamu Abbas, a lokacin taron karrama na 59 na jami’ar da aka gudanar ranar Asabar, 14 ga Disamba, 2024.

A cewar Farfesa Abbas, shugabannin jami’ar sun yanke shawarar dawo da shirin share fagen shiga Jami’a saboda dalilai guda biyu masu muhimmanci.

“Na farko, an lura da raguwa mai yawa a yawan dalibai masu rajista a fannonin Kimiyyar Lissafi, kuma shirin share fagen zai taimaka wajen magance wannan matsalar ta hanyar shirya dalibai don karatun kimiyya.”

Ya bayyana cewa, dalibai da dama suna fuskantar matsala wajen cika bukatun shiga fannonin kimiyya.

“Shirin share fagen shiga jami’a zai ba wa wadannan dalibai goyon bayan ilimi da ake bukata, wanda zai kara musu damar samun shiga jami’a.”

Farfesa Sagir ya kara da cewa, dawo da shirin zai inganta damammakin ilimi ga daliban BUK kuma zai bada gudunmawa ga ci gaban jami’ar.

taraba news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...
X whatsapp