fidelitybank

Jami’an tsaro sun kori gwamnan Edo mai barin gado daga ɗakin tattara sakamakon zaɓe

Date:

Jami’an ‘yansanda sun fitar da gwamnan jihar Edo Godwin Obaseki daga cikin ofishin hukumar zaɓen ƙasar, inda ake tattara sakamakon zaɓen gwamnan jihar da aka gudanar ranar Asabar.

Rahotoni sun ce cikin dare ne Mista Obaseki ya bayyana a cibiyar tattara sakamakon zaɓen da ke harabar hukumar tare da wasu jami’ai.

To sai dai babban mataimakin sifeton ‘yansandan ƙasar, DIG Frank Mba ya jagoranci fitar da gwamnan daga cikin ofishin hukumar tun cikin asubahin yau Lahadi.

Bayanai sun ce gwamnan ya je cibiyar tattara sakamakon ne domin bayyana ƙorafinsa kan zargin aikata ba daidai ba a sakamakon wasu ƙananan hukumomin jihar ciki har da ƙaramar hukumarsa ta Oredo.

Daga nan ne kuma jami’an ‘yansanda ƙarƙashin jagorancin DIG Mba da wasu jami’an soji suka isa cibiyar domin fito da gwamnan.

Jam’iyyar APC mai hamayya dai ta yi ƙorafi kan zuwan gwamnan cibiyar tattara sakamakon.

Nan gaba kaɗan ne hukumar zaɓen za ta fara aikin tattara sakamakon zaɓen daga ƙananna hukumomin jihar 18.

breaking news in nigeria today punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp