fidelitybank

Jami’an tsaro sun kori gwamnan Edo mai barin gado daga ɗakin tattara sakamakon zaɓe

Date:

Jami’an ‘yansanda sun fitar da gwamnan jihar Edo Godwin Obaseki daga cikin ofishin hukumar zaɓen ƙasar, inda ake tattara sakamakon zaɓen gwamnan jihar da aka gudanar ranar Asabar.

Rahotoni sun ce cikin dare ne Mista Obaseki ya bayyana a cibiyar tattara sakamakon zaɓen da ke harabar hukumar tare da wasu jami’ai.

To sai dai babban mataimakin sifeton ‘yansandan ƙasar, DIG Frank Mba ya jagoranci fitar da gwamnan daga cikin ofishin hukumar tun cikin asubahin yau Lahadi.

Bayanai sun ce gwamnan ya je cibiyar tattara sakamakon ne domin bayyana ƙorafinsa kan zargin aikata ba daidai ba a sakamakon wasu ƙananan hukumomin jihar ciki har da ƙaramar hukumarsa ta Oredo.

Daga nan ne kuma jami’an ‘yansanda ƙarƙashin jagorancin DIG Mba da wasu jami’an soji suka isa cibiyar domin fito da gwamnan.

Jam’iyyar APC mai hamayya dai ta yi ƙorafi kan zuwan gwamnan cibiyar tattara sakamakon.

Nan gaba kaɗan ne hukumar zaɓen za ta fara aikin tattara sakamakon zaɓen daga ƙananna hukumomin jihar 18.

today daily post news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp