fidelitybank

Jami’an tsaro sun ka mutane biyu da damfara a Zamfara

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara ta kama wani Lawali Musa mai shekaru 36 dan kauyen Jangebe da kuma Jamilu Isah mai shekaru 40 dan yankin Yar dole na kananan hukumomin Talata Mafara da Gusau na jihar bisa zargin karbar kudi.

Kamar yadda wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, SP Mohammed Shehu ya raba wa manema labarai a Gusau, ya ce an kama mutanen biyu ne biyo bayan korafin da mazauna kauyen ‘Yar Katsina da ke karamar hukumar Bungudu suka yi.

“A yayin da ake gudanar da bincike, babban wanda ake zargin, Lawali Musa ya amsa cewa ya karbo kudi naira miliyan biyar daga hannun al’umma da sunan taimaka musu wajen tura jami’an tsaro a yankinsu.

“A gefe guda kuma, wanda ake zargi na biyu, Jamilu Isah ya amsa cewa an saka kudi naira dubu dari takwas a asusun sa,” inji shi.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar ya ce har yanzu ana ci gaba da gudanar da bincike da nufin cafke wasu da ake zargi da aikata laifin.

Ya ba da tabbacin za a gurfanar da su gaban kotu bayan gudanar da cikakken bincike domin fuskantar fushin doka.

“Rundunar ta yi amfani da wannan kafar wajen nanata cewa tura jami’an tsaro zuwa kauyuka da al’ummomi kyauta ne kawai,” in ji shi, yana mai kira ga kowa da kowa da kada ya bari wani mutum ko gungun mutane su yaudare su da sunan tabbatar da tura sojoji na jami’an tsaro zuwa yankunansu.

SP Shehu ya shawarci al’umma da su tuntubi ‘yan sanda ko duk wata hukuma da abin ya shafa game da tsaron yankunansu.

network news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp