Rikicin shugabanci a majalisar dokokin jihar Legas da ke kudancin Najeriya ya ɗauki sabon salo, inda yanzu haka jami’an tsaro suka mamaye harabar ginin ‘yanmajalisar na tsaka da yin zama a yau Litinin.
Lamarin shi ne na baya-bayan nan a rikicin da ya dabaibaye majalisar tun bayan tsige Mudashiru Obasa a matsayin kakaki.
Kawo yanzu dai tsohon kakakin majalisar na ikirari cewa shi ne halastaccen kakakin majalisar bayan tsige shi, duk da maye gurbinsa da Meranda Mojisola.
Rahotonni sun nuna cewa jami’an tsaron sun rufe ofishin Meranda, da na mataimakinta.
Kazalika, an shafe lokaci kafin fara zaman na yau.