fidelitybank

Jami’an tsaro na farautar mai magana da yawun Gwamnan Kano

Date:

Akalla jami’an tsaro 40 ne daga Abuja ke ci gaba da neman mai magana da yawun Gwamna Abba Yusuf, Sanusi Bature Dawakin-Tofa kan labarin dakatar da Ganduje.

An tura mutanen IGP din ne daga Abuja domin kama Dawakin-Tofa bisa umarnin mukaddashin shugaban jam’iyyar All Progressives Congress, APC, Dr Abdullahi Ganduje.

Ganduje dai ya kai karar IGP ne kan cece-kucen da ya biyo bayan dakatar da shi da aka yi daga shiyyarsa ta Ganduje da ke karamar hukumar Dawakin-Tofa a jihar, inda ya zargi Kakakin Gwamnan da ya fito daga mazabarsa da kitsa rikicin siyasa.

Majiyoyin iyalan sun shaida wa manema labarai a ranar Talata cewa, tawagar ‘yan sandan da ke sanye da fararen kaya, sun sanya ido a kan gidan Dawakin-Tofa a ranar Litinin a wani mataki na gudanar da aikin nasu.

Daya daga cikin ‘ya’yan gidan da ya nemi a sakaya sunansa ya ce ‘yan sandan sirrin sun yi wa gidan farmaki sama da sau 5, lamarin da ya tsoratar da ‘yan gidan Dawakin-Tofa da suka hada da mata da ‘ya’ya tare da haifar da fargaba a unguwar.

Rundunar ‘yan sanda ta musamman ta IGP ta daura damarar kama Sanusi Dawakin-Tofa a cikin makonni biyun da suka gabata duk da umarnin da kotu ta bayar na hana su IGP, DSS, CP Kano da sauran hukumomin tsaro daga kamawa ko kuma musgunawa mai magana da yawun gwamnan.

Mai shari’a Amina Adamu Aliyu na babbar kotun jihar Kano a ranar Alhamis ta amince da bukatar da ta ke yi na hana ci gaba da farautar Sanusi Dawakin-Tofa har zuwa lokacin da za a ci gaba da sauraren wasu muhimman batutuwa game da hakkokinsa da aka tsara ranar 22 ga watan Janairun 2025.

Rikicin da ke tsakanin Dawakin-Tofa da Ganduje, ya samo asali ne tun shekaru tara da suka gabata, musamman a shekarar 2015, lokacin da Ganduje a matsayin zababben gwamna, ya bayar da umarnin a kamo Dawakin-Tofa saboda adawar da ya yi a lokacin zaben gwamna.

A kwanakin baya ne dai Ganduje ya kai karar IGP, inda ya zargi Dawakin-Tofa da cewa shi ne ke da alhakin dakatar da shi da shugabannin jam’iyyar APC Ganduje suka yi a watannin baya.

Sakamakon haka, an tattaro tawagar jami’an ‘yan sanda 40 daga sashin sa ido na IGP zuwa Kano da nufin cafke mai magana da yawun gwamnan.

Kokarin jin ta bakin kakakin rundunar ‘yan sandan hedikwatar ta kasa FPPRO ya ci turaJami’an

bbc news nigeria today live

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...
X whatsapp