Mai martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero, ya bukaci ‘yan sanda da sauran hukumomin tsaro da su kara kaimi wajen dakile munanan laifuka a jihar.
Sarkin ya bayyana haka ne a lokacin da ya karbi bakuncin sabon kwamishinan ‘yan sandan da aka nada a fadar sa a ranar Asabar.
Alhaji Ado Bayero, wanda Walin Kano, Alhaji Bashir Mahe ya wakilta, ya bukaci jami’an ‘yan sanda da su yi aiki da tsoron Allah da kuma aiki tukuru kamar yadda kundin tsarin mulkin tarayyar Najeriya ya tanada da kuma dokar ‘yan sanda ta shekarar 2020.
Ya bukaci hukumomin tsaro da su mutunta ‘yancin dan adam, bin doka da oda da kuma yin aiki bisa kyawawan halaye na kasa da kasa.
“Muna ba ku tabbacin goyon baya, addu’o’i, da taimakon dukkanin cibiyoyin gargajiya a fadin jihar,” in ji shi.
Tun da farko kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano, Mamman Dauda ya bayyana cewa manufarsa ta zuwa fadar sarkin ita ce don gabatar da kansa ga sarkin da kuma neman addu’a, hadin kai, da shawarwarin uba don ‘yan sandan jihar Kano yadda ya kamata.
“Za mu ci gaba da yin aiki gwargwadon iyawarmu don tabbatar da zaman lafiya a jihar,” in ji CP.