fidelitybank

Jami’an tsaro ku kara kaimi a bangaren tsaro – Sarkin Kano

Date:

Mai martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero, ya bukaci ‘yan sanda da sauran hukumomin tsaro da su kara kaimi wajen dakile munanan laifuka a jihar.

Sarkin ya bayyana haka ne a lokacin da ya karbi bakuncin sabon kwamishinan ‘yan sandan da aka nada a fadar sa a ranar Asabar.

Alhaji Ado Bayero, wanda Walin Kano, Alhaji Bashir Mahe ya wakilta, ya bukaci jami’an ‘yan sanda da su yi aiki da tsoron Allah da kuma aiki tukuru kamar yadda kundin tsarin mulkin tarayyar Najeriya ya tanada da kuma dokar ‘yan sanda ta shekarar 2020.

Ya bukaci hukumomin tsaro da su mutunta ‘yancin dan adam, bin doka da oda da kuma yin aiki bisa kyawawan halaye na kasa da kasa.

“Muna ba ku tabbacin goyon baya, addu’o’i, da taimakon dukkanin cibiyoyin gargajiya a fadin jihar,” in ji shi.

Tun da farko kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano, Mamman Dauda ya bayyana cewa manufarsa ta zuwa fadar sarkin ita ce don gabatar da kansa ga sarkin da kuma neman addu’a, hadin kai, da shawarwarin uba don ‘yan sandan jihar Kano yadda ya kamata.

“Za mu ci gaba da yin aiki gwargwadon iyawarmu don tabbatar da zaman lafiya a jihar,” in ji CP.

asuu news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp