fidelitybank

Jami’an tsaro ku kara kaimi a bangaren tsaro – Sarkin Kano

Date:

Mai martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero, ya bukaci ‘yan sanda da sauran hukumomin tsaro da su kara kaimi wajen dakile munanan laifuka a jihar.

Sarkin ya bayyana haka ne a lokacin da ya karbi bakuncin sabon kwamishinan ‘yan sandan da aka nada a fadar sa a ranar Asabar.

Alhaji Ado Bayero, wanda Walin Kano, Alhaji Bashir Mahe ya wakilta, ya bukaci jami’an ‘yan sanda da su yi aiki da tsoron Allah da kuma aiki tukuru kamar yadda kundin tsarin mulkin tarayyar Najeriya ya tanada da kuma dokar ‘yan sanda ta shekarar 2020.

Ya bukaci hukumomin tsaro da su mutunta ‘yancin dan adam, bin doka da oda da kuma yin aiki bisa kyawawan halaye na kasa da kasa.

“Muna ba ku tabbacin goyon baya, addu’o’i, da taimakon dukkanin cibiyoyin gargajiya a fadin jihar,” in ji shi.

Tun da farko kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano, Mamman Dauda ya bayyana cewa manufarsa ta zuwa fadar sarkin ita ce don gabatar da kansa ga sarkin da kuma neman addu’a, hadin kai, da shawarwarin uba don ‘yan sandan jihar Kano yadda ya kamata.

“Za mu ci gaba da yin aiki gwargwadon iyawarmu don tabbatar da zaman lafiya a jihar,” in ji CP.

latest news in lokoja, kogi state

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...
X whatsapp