fidelitybank

Jami’an So Safe Corps ta kama masu hakar ma’adanai a Ogun

Date:

Jami’an hukumar tsaro na So-Safe Corps mallakin jihar Ogun, sun kama wasu masu hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba har su 12 a yankin Ogun ta Gabas.

An kama mutanen 12 a tsakanin ranakun 28 zuwa 30 ga watan Satumba, “a lokacin da suke satar dukiyar gwamnatin jihar.”

Kakakin Rundunar So-Safe, Moruf Yusuf, ya shaida wa wakilinmu cewa, an tsare masu hakar ma’adinan ba bisa ka’ida ba ne a kauyen Abeku Adekanmbi da ke karamar hukumar Ijebu ta Arewa a jihar Ogun.

Yusuf ya bayyana cewa an kama mutanen 12 “a lokacin da suke satar albarkatun ma’adinai kamar gawayi da zinare a karkashin kasa.”

A cewarsa, Kwamandan So-Safe, Soji Ganzallo, ba tare da bata lokaci ba, ya ba da umarnin a mika rahoton binciken farko na wadanda ake zargin zuwa hedikwatar hukumar ta jihar da ke Abeokuta.

Ganzallo ya kuma bayar da umarnin a gurfanar da sauran masu laifin da suka tsere ta hanyar babura.

Tuni dai aka mika wadanda ake zargin zuwa hedikwatar ‘yan sanda ta Ijebu Igbo domin ci gaba da bincike tare da gurfanar da su gaban kuliya, in ji Yusuf.

www.leadership ng.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An gargadi al’umma su yi taka tsan-tsan da ambaliyar ruwan sama

Yayin da ake ci gaba da fuskantar saukar ruwan...

Gwamnatin Tarayya za ta gina hanyar sufurin jirgin ƙasa a Kano

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta samar da titin...

Abin da ya sa muke ci gaba da tsare Sowore – Ƴansanda

Kwamishinan ƴansanda mai kula da sashen kai ɗauki na...

INEC za ta bai wa ɗaurarru damar kaɗa ƙuri’a a lokacin zaɓuka

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta ta duba yiwuwar bai...

Mai ya jawo Matan Zamfara su ka yi zanga-zanga

Ɗaruruwan mata ne tsofaffi da masu shawarya suka gudanar...

Aƙalla mutane 24,000 ne suka ɓata saboda Boko Haram a Najeriya

Kungiyar Agaji ta Red Cross ta bayyana cewa aƙalla...

‘Yansanda ku gaggauta sakin Sowore – Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP, Peter...

PDP ta gargaɗi mambobinta kan goyon bayan Tinubu

Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta gargaɗi...

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...
X whatsapp