fidelitybank

Jami’an So Safe Corps ta kama masu hakar ma’adanai a Ogun

Date:

Jami’an hukumar tsaro na So-Safe Corps mallakin jihar Ogun, sun kama wasu masu hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba har su 12 a yankin Ogun ta Gabas.

An kama mutanen 12 a tsakanin ranakun 28 zuwa 30 ga watan Satumba, “a lokacin da suke satar dukiyar gwamnatin jihar.”

Kakakin Rundunar So-Safe, Moruf Yusuf, ya shaida wa wakilinmu cewa, an tsare masu hakar ma’adinan ba bisa ka’ida ba ne a kauyen Abeku Adekanmbi da ke karamar hukumar Ijebu ta Arewa a jihar Ogun.

Yusuf ya bayyana cewa an kama mutanen 12 “a lokacin da suke satar albarkatun ma’adinai kamar gawayi da zinare a karkashin kasa.”

A cewarsa, Kwamandan So-Safe, Soji Ganzallo, ba tare da bata lokaci ba, ya ba da umarnin a mika rahoton binciken farko na wadanda ake zargin zuwa hedikwatar hukumar ta jihar da ke Abeokuta.

Ganzallo ya kuma bayar da umarnin a gurfanar da sauran masu laifin da suka tsere ta hanyar babura.

Tuni dai aka mika wadanda ake zargin zuwa hedikwatar ‘yan sanda ta Ijebu Igbo domin ci gaba da bincike tare da gurfanar da su gaban kuliya, in ji Yusuf.

nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...
X whatsapp