Jami’an Amotekun Corps a jihar Ondo, sun kama wasu da ake zargi da hannu a kisan kiyashin da aka yi a cocin St. Francis Catholic Church, a ranar 5 ga watan Yuni, wanda maharan sun kashe mutane 40 tare da jikkata wasu kusan 60 a harin.
“Mun gano motar ta karshe da suka yi amfani da ita wajen gudanar da aikin, kuma mun kama wasu. Mun dawo da wasu muhimman abubuwa waɗanda muke aiki akai.
“Ba za mu tsaya ba har sai mun gano tushen wannan lamari kuma ina tabbatar da cewa za a gurfanar da wadanda suka aikata laifin da masu daukar nauyinsu,” in ji kwamandan Amotekun na jihar, Adetunji Adeleye.
Ya bayyana hakan ne yayin da yake gabatar da wasu mutane 71 da ake zargi da aikata laifuka a gaban manema labarai a Akure ranar Alhamis.
Ya ce, an kama wadanda ake zargin su 71 a cikin wannan wata da laifin satar shanu, fashi da makami, kungiyar asiri, garkuwa da mutane, safarar mutane da kuma satar babura na kasuwanci.
Adeleye ya ce, tuni rundunar ta kwato babura 31 da aka sace.