fidelitybank

Jamhuriyat Benin ta karbi allular rigakafin Maleriya

Date:

Mahukunta a Jamhuriyar Benin sun ce ƙasar za ta karɓi kashin farko na rigakafin zazzaɓin cizon sauro – cutar da ke kan gaba wajen haifar da mutuwar yara ƙanana a ƙasar, kuma nan ba da jimawa ba za a fara yin rigakafin.

Ministan lafiya na Benin, Benjamin Hounkpatin ya shaida wa manema labarai a filin jirgin sama na Cotonou cewa, maleriya cuta ce da ke yawan addabar mutane a ƙasar.

Ya ce gwamnati a hukumance, ta karɓi allurai 215,900 na rigakafin cutar.

A cewarsa za a soma ba da allurar nan da wasu ƴan watanni.

A ƙasar ta Benin, kashi 40 cikin 100 na masu zuwa asibiti da kashi 25 cikin 100 na mutanen da aka kwantar na da alaƙa da zazzabin cizon sauro, a cewar ministan.

Ya ce jarirai za su karɓi alluran sau huɗu – suna wata shida da wata bakwai da wata tara da kuma wata 18.

Benin ce ƙasar Afirka ta uku da ta samu alluran rigakafin maleriya bayan Kamaru da Saliyo, bayan da aka ƙaddamar da shirin a Ghana da Kenya da Malawi ƙarƙashin kulawar hukumar lafiya ta duniya bisa tallafin shirin kawance kan alluran rigakafi na GAVI.

An yi wa yara fiye da miliyan biyu rigakafin cutar a waɗannan ƙasashen Afirka uku abun da ya kawo raguwar mace-macen da ke da nasaba da maleriya, kamar yadda shirin GAVI ya bayyana.

A cewar WHO, kusan kowane minti guda, ana samun yara ƴan ƙasa da shekara biyar da ke mutuwa sanadin cutar.

asuu news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp