Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya ce, makwabciyar kasar Nijar za ta kare shi idan ya bar mulki.
A ranar Litinin, 29 ga watan Mayu ne Buhari zai bar fadar shugaban kasa ta Aso, inda zai mika wa zababben shugaban kasa, Bola Tinubu.
A yanzu ya yi alfahari da kyakkyawar alakarsa da Jamhuriyar Nijar.
A cewarsa, idan ‘yan Najeriya suka yi wa kasar wahalar rayuwa bayan bikin mika mulki, Nijar za ta kare shi.
Buhari ya bayyana hakan ne a yayin kaddamar da hedkwatar hukumar kwastam ta Najeriya da ke Abuja, ranar Talata.
Ya kuma kara tabbatar da cewa, zai koma yankin sa da ke Daura, wanda ke da nisa da Abuja amma kusa da Jamhuriyar Nijar.
“Na faɗi waɗannan ƴan abubuwan game da imanina, domin saura kwanaki shida kawai na tafi.
“Kuma ina kokarin yin nisa da Abuja yadda ya kamata. Na fito daga wani yanki mai nisa da Abuja.
“Na ce idan wani mai karfi ya motsa, ina da kyakkyawar alaka da makwabtana. Mutanen Nijar za su kare ni,” in ji Buhari.