Kamfanin rarraba wutar lantarki na Kano (KEDCO) ya sake yin kira ga jama’a da su kara sanya ido a cikin al’ummominsu a matsayin wani mataki na magance matsalar sata da kuma yawaitar barnar taransifoma a yankunansu.
Aminiya ta ruwaito cewa, kamfanin na DisCo ya dade yana korafin sata da barna, wanda ya kai asarar miliyoyin Naira.
KEDCO a cikin wata sanarwa da shugaban sashen sadarwa na kamfanin, Ibrahim Sani Shawai, ya fitar a ranar Alhamis, ya ce, matakin zai tabbatar da samar da wutar lantarki akai-akai ga kwastomomi.
“Wadanda ke lalata mana kayan aikinmu suna amfani da lokacin damina suna kutsawa cikin tiranfomarmu don lalata igiyoyi, satar mai da sauran kayayyaki masu daraja. Hadarin da ke tattare da irin wadannan ayyuka na jefa jama’a da ma masu aikata ta’asa cikin bala’i,” in ji wani bangare na sanarwar.,