fidelitybank

Jama’a sai sun taimaka za mu iya magance ta’addancin Najeriya – Ribadu

Date:

Mai ba shugaban kasa shawara kan tsaron Kasa, Malam Nuhu Ribadu, ya bayyana cewa ba za a iya samun nasarar yakar ta’addanci da aikata miyagun laifuka ba tare da hadin kai da goyon bayan ‘yan kasa ba.

Ribadu ya kuma yi kira ga ‘yan kasa da su gaggauta ba da rahoto ga hukumomin tsaro kan duk wani abu da ba su gamsu da shi ba.

Wannan na kunshe a cikin sakonsa na sabuwar shekara da Babban kwamanda na cibiyar kasa ta yaki da ta’addanci, Ofishin NSA, Manjo Janar Adamu Laka, ya sa wa hannu.

Ribadu ya tabbatar da cewa tare da hadin gwiwa, za a magance ta’addanci, tsattsauran ra’ayi da sauran manyan laifuka a shekara ta 2025.

Ya jaddada cewa hukumomin tsaro za su ci gaba da jajircewa wajen kare kasar.

“Tsaro hakkin kowa ne. Ba za a iya samun nasarar yakar ta’addanci da miyagun laifuka ba tare da hadin kai da goyon bayan ‘yan kasa ba. Saboda haka, ina rokon ku da ku gaggauta bayar da rahoto kan duk wani abu da ba ku amince da shi ba ko wani motsi da ba ku gamsu da shi ga hukumomin da suka dace. Idan kun ga wani abu, ku sanar,” in ji Ribadu.

Ya kuma tabbatar wa ‘yan Najeriya da cewa hukumomin tsaro za su ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da tsaro da kariyarsu.

labaran duniya na yau

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp