fidelitybank

Jakadiyar ECOWAS za ta gana da Tinubu kan makomar Nijar

Date:

Mataimakiyar sakataren harkokin ƙasashen Afirka ta Amurka, Molly Phee ta ziyarci Najeriya domin shiga tsakani kan rikicin shugabancin Nijar, wadda ke ƙarƙashin mulkin soji tun ranar 26 ga watan Yuli.

A cikin wata sanarwa da aka wallafa a shafin ma’aikatar harkokin wajen Amurka, ta nuna cewa Ms Phee za ta tattauna da shugaban Najeriya Bola Tinubu, tare da shugabannin ƙungiyar Ecowas kan rikicin siyasar Nijar.

Sanarwar ta ce an tsara ganawa tsakanin jakadiyar Amurkan da shugabanin ƙasashen ƙungiyar Ecowas ranar Litinin 10 ga watan Disamba domin tattauna batun.

“A lokacin ziyarar tata, za ta tattauna da shugabannin Afirka da Yamma, kan yadda Amurka za ta tallafa wajen maido da mulkin dimokraɗiyya a jamhuriyar Nijar, tare da inganta tsaro da zaman lafiya da ci gaban yankin, da kuma tabbatar da dimokraɗiyya a yankin sahel,” kamar yadda sanarwar ta nuna.

Ziyarar Ms Phee Najeriya na zuwa ne watanni huɗu bayan da sojojin Nijar ƙarƙashin jagorancin Janar Abdourahmane Tchiani suka kifar zaɓaɓɓiyar gwamnatin farar hula ta Mohamed Bazoum.

Juyin mulkin na ranar 26 ga watan Yuli ya sha suka da Allah wadai daga ƙasashen duniya, yayin da ƙasashen Yamma suka nuna goyon bayansu ga ƙungiyar Ecowas da ta AU, waɗanda suka nuna adwarsu ga juyin mulkin.

Inda ƙungiyar Ecowas ƙarƙashin jagorancin shugaban Najeriya Bola Tinubu ta ƙaƙaba wa Nijar jerin takunkuman karya tattalin arziki, don tilasta wa sojojin mayar da shugaba Bazoum kan karagar mulki.

www.nigerianews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp