Mataimakiyar sakataren harkokin ƙasashen Afirka ta Amurka, Molly Phee ta ziyarci Najeriya domin shiga tsakani kan rikicin shugabancin Nijar, wadda ke ƙarƙashin mulkin soji tun ranar 26 ga watan Yuli.
A cikin wata sanarwa da aka wallafa a shafin ma’aikatar harkokin wajen Amurka, ta nuna cewa Ms Phee za ta tattauna da shugaban Najeriya Bola Tinubu, tare da shugabannin ƙungiyar Ecowas kan rikicin siyasar Nijar.
Sanarwar ta ce an tsara ganawa tsakanin jakadiyar Amurkan da shugabanin ƙasashen ƙungiyar Ecowas ranar Litinin 10 ga watan Disamba domin tattauna batun.
“A lokacin ziyarar tata, za ta tattauna da shugabannin Afirka da Yamma, kan yadda Amurka za ta tallafa wajen maido da mulkin dimokraɗiyya a jamhuriyar Nijar, tare da inganta tsaro da zaman lafiya da ci gaban yankin, da kuma tabbatar da dimokraɗiyya a yankin sahel,” kamar yadda sanarwar ta nuna.
Ziyarar Ms Phee Najeriya na zuwa ne watanni huɗu bayan da sojojin Nijar ƙarƙashin jagorancin Janar Abdourahmane Tchiani suka kifar zaɓaɓɓiyar gwamnatin farar hula ta Mohamed Bazoum.
Juyin mulkin na ranar 26 ga watan Yuli ya sha suka da Allah wadai daga ƙasashen duniya, yayin da ƙasashen Yamma suka nuna goyon bayansu ga ƙungiyar Ecowas da ta AU, waɗanda suka nuna adwarsu ga juyin mulkin.
Inda ƙungiyar Ecowas ƙarƙashin jagorancin shugaban Najeriya Bola Tinubu ta ƙaƙaba wa Nijar jerin takunkuman karya tattalin arziki, don tilasta wa sojojin mayar da shugaba Bazoum kan karagar mulki.