Jakadan kasar Kenya a Najeriya, Dr. Wilfred Machege, ya yanke jiki a cikin gidansa ya mutu nan take.
Machege ya kammala cin abincin rana a ranar Asabar, kuma ya fadi ne a yayin da matarsa ke tare da shi.
An hanzarta garzayawa da shi wani asibiti da ke cikin garin Abuja, amma a ka tabbatar da mutuwarsa.
Vanguard ta rawaito cewa, yayin tabbatar da rasuwar Amb. Machage, shi ne babban sakataran Jakada, wanda Macharia Kamau, ya ce, ma’aikatar da kasar sun rasa jajirtaccen shugaba.