fidelitybank

Jagoran Venezuela ya yi balaguro zuwa Spain

Date:

Gwamnatin Venezuela ta ce ɗan takarar shugaban ƙasar na jam’iyyar adawa, Edmundo González, ya fice daga ƙasar zuwa Sifaniya domin neman mafaka.

Cikin wani saƙo da mataimakiyar shugaban ƙasar, Delcy Rodríguez, ta wallafa a shafinta na sada zumunta, ta ce ”bayan neman zaman gudun hijira da ya yi bisa raɗin kansa a ofishin jakadancin Sifaniya da ke birnin Caracas a kwanakin da suka gabata, mista Gonzalez ya nemi gwamnatin Sifaniya ta ba shi mafakar siyasa”.

Ta ƙara da cewa gwamnatin Venezuela ta amince da ficewarsa daga ƙasar, kuma tuni ya yi hakan.

Ministan harkokin wajen Sifaniya, José Manuel Albares, ya ce Mista González ya fice daga Venezuela ne bisa raɗin kansa, kuma ya fice ne a jirgin rundunar sojin Sifaniya.

Mista González ya kasance yana wasan ɓuya da jami’an tsaro a Venezuela, bayan da aka bayar da sammacin kama shi sakamakon zaɓen shugabar ƙasar da ya gabata mai cike da taƙaddama.

Hukumar zaɓen ƙasar dai ta ayyana shugaba Nicolás Maduro a matsayin wanda ya lashe zaɓen, duk da ayyana samun nasara da mista González ya yi, gabanin sanarwar hukumar zaɓen ƙasar.

legit news.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...
X whatsapp