Gwamnatin Venezuela ta ce ɗan takarar shugaban ƙasar na jam’iyyar adawa, Edmundo González, ya fice daga ƙasar zuwa Sifaniya domin neman mafaka.
Cikin wani saƙo da mataimakiyar shugaban ƙasar, Delcy Rodríguez, ta wallafa a shafinta na sada zumunta, ta ce ”bayan neman zaman gudun hijira da ya yi bisa raɗin kansa a ofishin jakadancin Sifaniya da ke birnin Caracas a kwanakin da suka gabata, mista Gonzalez ya nemi gwamnatin Sifaniya ta ba shi mafakar siyasa”.
Ta ƙara da cewa gwamnatin Venezuela ta amince da ficewarsa daga ƙasar, kuma tuni ya yi hakan.
Ministan harkokin wajen Sifaniya, José Manuel Albares, ya ce Mista González ya fice daga Venezuela ne bisa raɗin kansa, kuma ya fice ne a jirgin rundunar sojin Sifaniya.
Mista González ya kasance yana wasan ɓuya da jami’an tsaro a Venezuela, bayan da aka bayar da sammacin kama shi sakamakon zaɓen shugabar ƙasar da ya gabata mai cike da taƙaddama.
Hukumar zaɓen ƙasar dai ta ayyana shugaba Nicolás Maduro a matsayin wanda ya lashe zaɓen, duk da ayyana samun nasara da mista González ya yi, gabanin sanarwar hukumar zaɓen ƙasar.