fidelitybank

Jagoran Hezbollah na jawabi a kan makomar Lebanon a yakar Isra’ila

Date:

Jagoran Hezbollah Hassan Nasrallah yana gabatar da jawabi tsawon ‘yan mintuna kalilan yanzu.

Yana yabawa hare-haren da Hamas ta kai na ranar 7 ga watan Oktoba a kan Isra’ila, wanda ya yi sanadin kashe fiye da mutum 1,400.

Wakilin BBC a yankin Gabas ta Tsakiya na kallon jawabin kuma za mu kawo muku sharhi kan abin da ya ce da kuma abin da hakan ke nufi kan yakin da ake ci gaba da gwabzawa.

A yanzu kuma, ga bayani game da jagoran wanda ba a cika gani a bainar jama’a ba, na kungiyar da Birtaniya da Amurka da Isra’ila da kuma karin wasu kasashe, suka ayyana a matsayin ta ‘yan ta’adda.

Malamin mai bin mazhabar Shi’a, shi ne ke jagorantar Hezbollah tun daga 1992, kuma Nasrallah ya ba da gagarumar gudunmawa wajen mayar da ita kungiyar siyasa da runduna mai karfin soja.

Yana da alaka ta kukut da kasar Iran da kuma jagoran addininta, Ayatollah Ali Khamenei, tun daga 1981, lokacin da jagoran addinin Iran na farko, Ayatollah Ruhollah Khomeini, ya nada shi wakilinsa na musamman a Lebanon.

Tsawon shekaru kenan, ba a ga Nasrallah a bainar jama’a ba, kamar yadda ake zargi saboda tsoron kada Isra’ila ta hallaka shi.

Sai dai ya kasance abin matukar martabawa daga Hezbolla kuma yana gabatar da jawabansa ta talbijin a duk mako.

leadership news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp