Hukumar zabe ta kasa INEC ta ce babban zaben shekarar 2023 za a fara gudanar da na shugaban kasa da mataimakin sa a ranar 18 ga watan Fabrairu, sai na ‘yan majalisar wakilai da dattijai da na sanatoci duk za a yi su ne a rana daya.
Jaridar Leadership ta rawaito cewa, sanarwar ta cigaba da cewar zaben gwamnoni da ‘yan majalisar dokoki na jahohi kuma zai kasance ranar 4 ga watan Maris na shekarar 2023.
Wadanda suka samu nasara kuma za a rantsar da su a ranar 29 ga watan Mayun 2023.