fidelitybank

Jadawalin gasar Firimiyar kasar Ingila makon farko

Date:

Ranar Juma’a 16 ga watan Agusta

  • Manchester United da Fulham

Ranar Asabar 17 ga watan Agusta

  • Ipswich Town da Liverpool
  • Arsenal da Wolverhampton
  • Everton da Brighton
  • Newcastle United da Southampton
  • Nottingham Forest da Bournemouth
  • West Ham United da Aston Villa

Ranar Lahadi 18 ga watan Agusta

  • Brentford da Crystal Palace
  • Chelsea da Manchester City

Ranar Litinin 19 ga watan Agusta

  • Leicester City da Tottenham

Wasu mahimman batuwan da suka shafi Premier League 2024/25

Manchester City za ta buga wasa biyu daga bakwai kafin Champions League, wadda za ta yi uku a Etihad da Aston Villa da Arsenal da kuma Liverpool.

Wasa mai nisa da za a buga shi ne mil 200 ranar 26 ga watan Disamba da Arsenal za ta ziyarci Newcastle United a St James Par.

Makon karshe da za a fafata don lashe FA Cup, shi ne Asabar 17 ga watan Mayu, ranar ba za a kara a Premier League ba.

A mako na uku a kakar da za a fara Aston Villa za ta je gidan Tottenham, yayin da Liverpool za ta karbi bakuncin Chelsea a Anfield.

A wasan mako na hudu kuwa Manchester City za ta je gidan Tottenham daga nan ta kece raini da Liverpool.

Manchester United za ta karbi bakuncin Liverpool ikafin hutun kalandar Fifa a Satumba, Arsenal ta ziyarci Tottenham ana kammala hutun.

Everton za ta buga wasan karshe a Goodison Park – daga nan ta koma Bramley-Moore Dock – za ta fara karawa da Southampton ranar Lahadi 18 ga watan Mayu a makon da za a buga wasan karshe a FA Cup.

Yaushe za a fara wasannin Premier League 2024/25?

Za a fara Premier League kakar 2024-25 ranar Juma’a 16 ga watan Agusta a karkare ranar Lahadi 25 ga watan Mayun 2025 da yin wasa 10 rana daya a lokaci tare.

Za a yi mako 33 da yin karawa a tsakiyar mako karo hudu da daya a lokacin Kirsimeti, wato ranar 26 ga watan Disamba.

Za a yi hutun Fifa da ta kan bayar cikin watan Satumba da Nuwamba da kuma watan Maris, yayin da za a buga wasan zagaye na uku a FA Cup a makon nin Janairu.

Domin samun buga karawar tsakiyar makon Agusta, babu hutu a lokacin hunturu, yayin da ba za a maimaita wasa ba kwana daya kafin Kirsimeti da aka yi tsakanin Wolves da Chelsea ba a kakar da ta wuce, karon farko tun 1995.

An sanar da kungiyoyin da za su buga Premier League cewar ba wadda za ta buga wasa biyu a jere kasa da awa 60 a tsakanin Kirsimerti da sabuwar shekara.

Ukun da suka samu shiga Premier League da wadanda suka yi ban kwana

Kungiyoyin ukun da suka hauro zuwa Premier League, sun hada da Leicester City, wadda ta lashe Championship da kuma Ipswich ta biyu.

Ta ukun ita ce Southampton, wadda ta yi nasara a kan Leeds United a karawar cike gurbi.

Wadanda suka yi ban kwana da wasannin da aka kammala sun hada da Luton Town da Burnley da kuma Sheffield United. In ji BBC.

news nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp