fidelitybank

Iyalan ‘Yan Sanda sun karbi Naira biliyan 2

Date:

Babban sifeton ‘yan sandan kasar nan, Kayode Egbetokun, ya bayar da chekin naira biliyan 2.08 ga iyalan ‘yan sandan da suka mutu a bakin aiki cikin shekara biyar da suka gabata.

Cikin wata sanarwa da mai magana yawun rundunar ‘yan sandan ƙasar, Olumuyiwa Adejobi, ya fitar ya ce an bayar da chekin kuɗin ga mutum 785 da za su amfana da kuɗaɗen.

“Rundunar ‘yan sandan Najeriya, ta hanyar ofishin kula da inshora, ya samu damar warware haƙƙoƙin mamata kusan 2,533 wanda ya kama kusan naira biliyan 6.01 tsakanin watan Yunin 2023 zuwa yau”, in ji sanarwar.

Babban sifeton ‘yan sandan ya kuma yaba wa shugaban ƙasar Bola Tinubu, saboda sanya walwalar ‘yan sanda cikin manyan abubuwan da gwamnatinsa ta sa a gaba.

A Najeriya dai iyalan jami’an tsaro kan shiga tasku bayan mutuwar iyayensu ko mazajensu waɗanda suka sadaukar da rayukansu wajen bauta wa ƙasar.

tribune newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp