fidelitybank

Iya wa’adi daya ya ishe ni a mulkin Najeriya – Peter Obi

Date:

Tsohon ɗan takarar shugabancin Najeriya a jam’iyyar Labour, Peter Obi ya ce idan ya samu nasarar zama shugaban ƙasar, wa’adi ɗaya na shekara huɗu kawai zai yi kamar yadda ya yi alƙawari.

Obi ya bayyana haka ne a shafinsa na X, inda ya ce ko tsohon shugaban Amurka, Abraham Lincoln wa’adi ɗaya ya yi na shekara huɗu, “sannan John F. Kennedy bai ma ƙarasa wa’adi ɗaya ba, amma ana cigaba da tunawa da su a matsayin shugabanni masu adalci.”

Ya ce ko a Afirka, Nelson Mandela ya zama abin koyi a duniya wajen shugabanci na adalci, “amma wa’adi ɗaya kawai ya yi.”

“Ba daɗewa a ofis ba ne ke alamta nasara, irin ayyukan da shugaba ya yi ne za a riƙa tunawa. Saboda haka ne nake sake nanata alƙawarin da na yi cewa wa’adi ɗaya na shekara huɗu kawai zan yi idan na zama shugaban Najeriya,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa ya san ƴan Najeriya ba su cika yarda da maganar ƴan siyasa ba, “amma duk da haka akwai masu cika alƙawari.”

“Na ga wani yana rubuta cewa ko da me zan rantse ba zai yarda cewa wa’adi ɗaya zan yi ba, wani kuma ya ce duk wanda ya ce wa’adi ɗaya zai yi ya je asibitin ƙwaƙwalwa.”

Obi ya ce ya fahimci abin da suke nufi, amma a cewarsa, yana da tarihi mai kyau wajen cika alƙawari tun daga lokacin da ya fara siyasa a Anambra, inda ya ce wata 48 sun isa duk wani shugaba da ya shirya mulki ya yi abin da ya dace.

“Idan na zama shugaban Najeriya a wa’adi ɗaya zan magance matsalar tsaro, zan yaƙi da talauci in inganta aikin gwamnati, sannan zan fifita ɓangaren ilimi da kiwon lafiya, sannan in yaƙi cin hanci da rashawa. Sannan uwa-uba zan inganta ɓangaren noma ta hanyar amfani da kimiyya da fasaha domin Najeriya ta zama ƙasa mai ciyar da kanta da wasu ƙasashen.”

nigerian news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iya wa’adi daya ya ishe ni a mulkin Najeriya – Peter Obi

Tsohon ɗan takarar shugabancin Najeriya a jam'iyyar Labour, Peter...

Luis Diaz ya zaba wa kansa makoma da ya bar Liverpool – James

Kyaftin din Colombia, James Rodríguez, ya dage cewa dan...

Ka fito ka baiwa Matawalle hakuri ko ka fuskanci fushin kotu – Shinkafi

Wani mai fafutukar kare hakkin bil’adama, Dakta Suleiman Shuaibu...

Liverpool za su sayar da ‘yan wasa uku su dauki Isak

Liverpool a shirye take ta sayar da matasan yan...

Ba zamu daga wa Hamas kafa ba har sai an saki mutanen mu – Netanyahu

Firaiministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, ya yi dogon...

Za mu gyara tsarin Maiduguri saboda ambaliya – Zulum

Gwamnan jihar Borno Babagana Umara Zulum ya ce, gwamnatinsa...

Dubban mutane sun yi zanga-zangar goyon bayan Falasɗinawa a Australia

Dubban mutane ne suka gudanar da zanga-zangar goyon bayan...

Mata da kanan Yara ne Ambaliya ta daidaita a jihohi 19 – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa, NEMA, ta...

Facebook ya ƙi amincewa da tsare-tsaren Turai na amfani da AI

Wasu muhimman tsare-tsare na dokokin Tarayyar Turai kan amfani...

Ranar 18 za a fara rajistar zabe – INEC

Hukumar zaɓe mai zaman kanta, INEC ta sanar da...

Trump ya tura jiragen ruwa na yaki masu dauke da makaman nukiliya kusa da Rasha

Shugaba Trump ya ce, ya umarci a matsar da...

Amnesty na tuhumar gwamnatin Najeriya kan bacewar Dadiyata

Ƙungiyar Amnesty International ta yi Allah-wadai da sakacin da...
X whatsapp