Faransa ta yi watsi da buƙatar Ivory Coast na ɗaukar hayar tsohon kocinta Herve Renard domin jagorantar tawagar ƙasar ta ƙarasa gasar Afcon ta 2023 da ke gudana.
Dan shekara 55 din yanzu shi ke jagorantar tawagar matan Faransa, sai dai hukumar kwallon ƙafa ta Faransa ta yi watsi da wannan buƙata ta aron kocin.
Masu masaukin bakin sun kai zagaye na biyu na gasar sai dai sun kori kocinta Jean Louis Gasset a ranar Laraba, biyo bayan rashin nasarar da ta yi sau biyu a matakin rukuni.
Bayan tafiyar Gasset tawagar Elephants ta samu damar zagaye na 16 a matsayin ƙungiyoyi huɗu da aka yi wa alfarma, yanzu kuma za ta fafata da Senegal da ke riƙe da kofin.