An nada dan kasar Faransa Jean-Louis Gasset, a matsayin sabon kocin kasar Ivory Coast kan kwantiragin watanni 12 na farko.
Kasar da ke yammacin Afirka za ta karbi bakuncin gasar cin kofin nahiyar Afirka a shekarar 2023 a watan Yunin shekara mai zuwa, kuma kocin mai shekaru 68 na da zabin karin shekara a yarjejeniyar.
Ya maye gurbin dan kasar Patrice Beaumelle, wanda ba a sabunta kwantiraginsa ba, bayan da Giwayen suka yi rashin samun gurbin shiga gasar cin kofin duniya, kuma suka yi rashin nasara a gasar cin kofin duniya da aka yi a Kamaru a farkon wannan shekarar.
Gasset ya yi aiki a matsayin mataimaki ga Laurent Blanc lokacin yana kocin Faransa daga 2010-12 da kuma Paris St-Germain. Ya jagoranci kungiyoyin Faransa Montpellier, Caen, Istres, Saint-Etienne da Bordeaux, wadanda Gasset ya bar kungiyar a karshen kakar wasan data gabata.