fidelitybank

Italiya ta baiwa Najeriya allurar Korona sama da miliyan 3

Date:

Gwamnatin tarayya a ranar Litinin ta karɓi sabbin allurai 3,002,400 na allurar rigakafin Covid-19 guda ɗaya na Johnson & Johnson wanda gwamnatin Italiya ta bayar.

Da yake karbar allurar a madadin gwamnatin tarayya a Abuja, babban sakataren hukumar kula da lafiya matakin farko ta kasa (NPHCDA), Dr Faisal Shuaib, ya ce, za a tura allurar yadda ya kamata a yaki da cutar.

A cewarsa, “Ya zuwa yau 11 ga Afrilu, 2022, mun yi wa mutane 13, 588, 718 allurar riga-kafi.

Ya ce, mutane 23,012,700 ne suka dauki kashi na farko na rigakafin; wanda ke wakiltar kashi 18 cikin ɗari na jimlar yawan mutanen da suka cancanta.

Ya ce: “Na gode da kasancewa tare da mu don karba a madadin gwamnatin tarayya alluran rigakafin Johnson da Johnson Covid-19 miliyan uku da dubu 2 da dari hudu da gwamnatin Italiya ta bayar.

“Ina so in gode wa gwamnatin Italiya, saboda wannan gudummawar da ta yi daidai da kiran da duniya ta yi na samun daidaitattun allurar rigakafin Covid-19. Hakan kuma na nuni ne da irin gaskiya da jajircewar gwamnatin Italiya da tawagar kasashen Turai kan kokarin da duniya ke yi na dakile wannan annoba, domin al’ummar duniya su koma hanyar rayuwa ta al’ada.

A nasa jawabin, jakadan Italiya a Najeriya, Stefano De Leo, ya bayyana cewa, Italiya ta ci gaba da jajircewa tare da sauran mambobin Tarayyar Turai, don tallafa wa Najeriya bukatar allurar rigakafin, da nufin taimakawa wajen fadada yaduwar allurar rigakafi a duniya.

bbc nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dangantaka tsakanin Amurka da Canada ta yi tsami

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce zai yanke dukkan...

An yi jana’izar Kwamandojin sojinta da masana nukiliyar Iran da Isra’ila ta kashe

Iran ta gudanar da jana'izar mutum 60, ciki har...

Za a binne Attaijirin dan kasuwar nan na Kano Dantata a Dubai

Allah ya yi wa attajirin ɗan kasuwar nan na...

Dalori ne ya maye gurbin Gnaduje a shugabancin APC

Mataimakin shugaban jam'iyyar APC na yankin arewa, Ali Bukar...

IGP ya ba da umarnin bincike kan bidiyon ƙorafin wani tsohon ɗansanda

Babban Sufetan ‘Yan Sandan Najeriya, Kayode Adeolu Egbetokun, ya...

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar ƙasar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karo na farko

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karon farko...

Sojoji na zaman makoki na kwanaki 3 bayan an kashe Jami’ai 17

Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na...

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...

Sojoji sun mayar da martani kan ‘Yan ta’addan Neja

Dakarun Sojin Saman kasar nan, sun ce sun ƙaddamar...

Kotu ta yanke wa Matashin da ya kashe Budurwarsa hukuncin kisa

Kotun babban birnin jihar Nasarawa ta yanke wa wannan...
X whatsapp