fidelitybank

Italiya ta baiwa Najeriya allurar Korona sama da miliyan 3

Date:

Gwamnatin tarayya a ranar Litinin ta karɓi sabbin allurai 3,002,400 na allurar rigakafin Covid-19 guda ɗaya na Johnson & Johnson wanda gwamnatin Italiya ta bayar.

Da yake karbar allurar a madadin gwamnatin tarayya a Abuja, babban sakataren hukumar kula da lafiya matakin farko ta kasa (NPHCDA), Dr Faisal Shuaib, ya ce, za a tura allurar yadda ya kamata a yaki da cutar.

A cewarsa, “Ya zuwa yau 11 ga Afrilu, 2022, mun yi wa mutane 13, 588, 718 allurar riga-kafi.

Ya ce, mutane 23,012,700 ne suka dauki kashi na farko na rigakafin; wanda ke wakiltar kashi 18 cikin ɗari na jimlar yawan mutanen da suka cancanta.

Ya ce: “Na gode da kasancewa tare da mu don karba a madadin gwamnatin tarayya alluran rigakafin Johnson da Johnson Covid-19 miliyan uku da dubu 2 da dari hudu da gwamnatin Italiya ta bayar.

“Ina so in gode wa gwamnatin Italiya, saboda wannan gudummawar da ta yi daidai da kiran da duniya ta yi na samun daidaitattun allurar rigakafin Covid-19. Hakan kuma na nuni ne da irin gaskiya da jajircewar gwamnatin Italiya da tawagar kasashen Turai kan kokarin da duniya ke yi na dakile wannan annoba, domin al’ummar duniya su koma hanyar rayuwa ta al’ada.

A nasa jawabin, jakadan Italiya a Najeriya, Stefano De Leo, ya bayyana cewa, Italiya ta ci gaba da jajircewa tare da sauran mambobin Tarayyar Turai, don tallafa wa Najeriya bukatar allurar rigakafin, da nufin taimakawa wajen fadada yaduwar allurar rigakafi a duniya.

thisday news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp