Wani kazamin fadan da ya barke tsakanin bangarorin ‘yan ta’adda da ke gaba da juna ya yi sanadiyar mutuwar mayakan Boko Haram 15, yayin da wasu ‘yan kungiyar IS da ke yankin yammacin Afirka, ISWAP su biyar suka samu raunuka a garin Tumbum-Kare na kasar Kamaru.
Zagazola Makama, kwararre ne kan yaki da ta’addanci da tayar da kayar baya a tafkin Chadi, ya sanar da hakan ta hanyar wani sakon da ya wallafa a shafinsa na X ranar Laraba.
Makama ya ce wasu majiyoyin leken asiri sun sanar da shi cewa arangama ta faru ne a lokacin da kungiyar ISWAP ta kai wani hari na hadin gwiwa kan mayakan Boko Haram masu biyayya ga bangaren Bakura Buduma.
A cewar masanin tsaro, harin da aka kai da nufin tabbatar da mamaya, ya janyo hasarar dimbin yawa a bangaren Boko Haram, inda mayakan ISWAP suka kwace wasu makamai da ba a bayyana adadinsu ba a yayin arangamar.
Wannan lamari dai shi ne na baya bayan nan a rikicin da ya barke tsakanin kungiyoyin biyu.
Kasashen biyu dai sun yi takun saka mai zafi a kan albarkatun kasa, da ikon mallakar yankuna, da kuma tasiri a yankin tafkin Chadi.
Makama ya kara da cewa, majiyoyin leken asiri sun ce fadan ya kara kamari a ‘yan watannin nan, yayin da kungiyoyin biyu ke neman fadada sansanonin su a yankin, inda tuni kungiyar Boko Haram ta yi galaba a kan ISWAP.