Dakarun daular Islama ta yammacin Afirka (ISWAP) ta kashe wasu jamiāan kungiyar Boko Haram guda biyu, Abou Hamza (Munzir) da Abou Ibrahim (Nakib), a lokacin da suka kai farmaki a tsakiyar dare a ranar 17 ga Satumba, 2022. a Gaizuwa a karamar hukumar Bama.
An tattaro cewa ISWAP ce ta kashe kwamandojin biyun a cikin rudani, yayin da aka gano gawarwakinsu a gidajensu da sanyin safiyar ranar 18 ga watan Satumba.
Zagazola Makama, kwararre kan yaki da tada kayar baya a yankin tafkin Chadi, ya ce, kafin harin na baya-bayan nan, kungiyar Boko Haram ta sha alwashin daukar fansa kan kashe ‘yan ta’adda 29 da suka hada da wani babban kwamandan da ‘yan ta’addar ISWAP suka yi wa kwanton bauna.
Wata majiya mai tushe ta bayyana cewa daga baya āyan Boko Haram sun gayyaci mayaka sama da 70 daga sassan Mafa, Karkut, Shiwai, lawe Kanuriye, Kirwa da Amtifur domin su taimaka musu wajen aiwatar da ramuwar gayya kan ISWAP.
Majiyar ta ce āSun kasu kashi biyu kafin su tashi daga Gaizuwa.
āAmma kafin su isa yankin ISWAP, sai suka sake fuskantar wata mummunar wuta daga ISWAP wadanda tuni suka san shirinsu, inda suka kashe wadanda ba a tantance adadinsu ba.
āMayakan Boko Haram sun fantsama ta bangarori daban-daban inda aka kashe da dama tare da jikkata wasu kuma an kama su da rai tare da kwace makamansu,ā in ji shi.
Kungiyar ta ISWAP dai ta kai hare-hare da dama a kan kungiyar ta Boko Haram a cikin makonnin da suka gabata lamarin da ya jefa Boko Haram cikin wani hali na rashin tabbas.