Ƙungiyar ISWAP ta ɗauki alhakin kisan mutum 26 a wani hari da ta kai jihar Borno da ke arewa maso gabashin Najeriya.
Ƙungiyar ta yi wannan iƙirari ne a shafin Telegram.
Lamarin ya faru ne ranar Litinin bayan da wata mota ta taka bam a gefen hanya kusa da iyaka da Kamaru a jihar ta Borno.
Hakan na zuwa ne kimamin mako biyu bayan da wata motar bas ta taka wani abin fashewa da aka binne a yankin, abin da ya janyo mutuwar fasinjoji takwas da kuma raunata wasu 11.
Ƙungiyar Boko Haram da ISWAP sun shafe tsawon shekara 15 suna kai hare-hare da kuma artabu da jami’an tsaron Najeriya a arewa maso gabas.
Sun sha amfani da abubuwan fashewa wajen afkawa fararen hula da kuma jami’an tsaro.