Da sanyin safiyar Asabar ne wasu ‘yan ta’addan da suka fito daga yankin yammacin Afirka ta ISWAP suka kai wani kazamin hari a garin Geidam da ke jihar Yobe, inda suka kashe wani mazaunin garin tare da yin barna mai yawa kamar yadda majiyoyi da dama suka bayyana.
An fara kai harin ne da misalin karfe 3:30 na safe lokacin da maharan suka far wa garin, inda suka rika harbin bama-bamai ba gaira ba dalili tare da tsoratar da mazauna garin.
Majiyoyin leken asiri sun bayyanawa wani kwararre a fannin yaki da ‘yan ta’adda Zagazola Makama cewa maharan sun lalata kadarori tare da kona wasu motoci biyu na jami’an hukumar kwastam ta Najeriya.
An ce mayakan sun lalata kabarin Khalifah Ayiloma da ke unguwar Kolori, inda suka cinnawa kabarin wuta.
Sun kuma kai hari gidan wani mai gadin dare Dahiru Muhammadu mai shekaru 60 da ke kusa da Geidam Polytechnic. Muhammadu ya samu rauni a wuyansa, inda aka garzaya da shi asibitin kwararru na Geidam, inda daga baya aka tabbatar da mutuwarsa.