fidelitybank

Isra’ilawa sun mutu bayan harin roka daga Hezbolah

Date:

Jami’an Isra’ila sun ce an kashe fararen hularta uku a wani hari da aka kai kan iyakar Jordan da Gaɓar Yamma.

Rahotonni sun ce maharin – wanda tuni sojojin Isra’ila suka kashe – direban motar dakon kaya ne, wanda ya taso daga Jordan, sannan ya tsaya a shingen binciken ababen hawa ya kuma buɗe wuta bayan ya sauko daga motar.

Ma’aikatan lafiya sun ce mutanen uku da aka kashe maza ne masu shekaru aƙalla 50, kamar yadda kafofin yaɗa labaran Isra’ila suka ruwaito.

Ƙasar Jordan ta ce ta ƙaddamar da bincike tare da rufe babbar gadar King Hussein, da ke mashigar Gaɓar Yamma, inda abun ya faru.

Lamarin ya faru ne a yankin da Isra’ila ke iko da shi, kuma nan ne motocin Jordan ɗauke da kaya ke bi don shiga Gaɓar Yamma.

Mashigar ta kasance ita kaɗai ce mashiga a hukumance tsakanin Gaɓar Yamma da Jordan.

Wannan batu na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da zaman ɗarar da fargaɓar ɓarkewar yaƙi a yankin Gabar ta Tsakiya.

Ko a cikin daren da ya gabata ma an samu musayar hare-haren makamai masu linzami tsakanin Isra’ila da ƙungiyar Hezbolla ta Lebanon.

legit.ng.news.

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp