Jami’an Isra’ila sun ce an kashe fararen hularta uku a wani hari da aka kai kan iyakar Jordan da Gaɓar Yamma.
Rahotonni sun ce maharin – wanda tuni sojojin Isra’ila suka kashe – direban motar dakon kaya ne, wanda ya taso daga Jordan, sannan ya tsaya a shingen binciken ababen hawa ya kuma buɗe wuta bayan ya sauko daga motar.
Ma’aikatan lafiya sun ce mutanen uku da aka kashe maza ne masu shekaru aƙalla 50, kamar yadda kafofin yaɗa labaran Isra’ila suka ruwaito.
Ƙasar Jordan ta ce ta ƙaddamar da bincike tare da rufe babbar gadar King Hussein, da ke mashigar Gaɓar Yamma, inda abun ya faru.
Lamarin ya faru ne a yankin da Isra’ila ke iko da shi, kuma nan ne motocin Jordan ɗauke da kaya ke bi don shiga Gaɓar Yamma.
Mashigar ta kasance ita kaɗai ce mashiga a hukumance tsakanin Gaɓar Yamma da Jordan.
Wannan batu na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da zaman ɗarar da fargaɓar ɓarkewar yaƙi a yankin Gabar ta Tsakiya.
Ko a cikin daren da ya gabata ma an samu musayar hare-haren makamai masu linzami tsakanin Isra’ila da ƙungiyar Hezbolla ta Lebanon.