fidelitybank

Isra’ila ta ƙaddamar da harin ramuwar gayya a kan Iran

Date:

Isra’ila ta ce ta kai wasu jerin hare-hare kan wasu wuraren aikin soja a Iran, a matsayin martani ga abin da ta kira ci gaba da kai hare-hare kan Isra’ila da Iran da kawayenta ke yi.

Kakakin sojin Isra’ila Daniel Hagari, ya ce ramakon tamkar wani nauyi ne da ya rataya a kan kasar, biyo bayan harba makami mai linzami kusan dari biyu da Iran ta harba masu a makonni uku da suka wuce.

Kamfanin dillancin labarai na Iqna ya ce an kai hari kan wasu sansanonin soji a yamma da kudu maso yammacin Tehran babban birnin kasar Iran.

Wakilin BBC a birnin Kudus ya ce Isra’ila ta takaita hare-haren na kan wuraren soji kadai kuma ba ta kai hari kan tashoshin nukiliya ko matatun man fetur ba.

An rawaito wani babban jami’in Iran na cewa za su mayar da zazzafan martani a lokacin da ya dace

Kasadar Iran ta kai wa Isra’ila hari bayan yin illa ga ƙawayenta
4 Oktoba 2024

An kuma bayar da rahoton tashin bama-bamai a Damascus babban birnin kasar Syria.

Kamfanin dillancin labaran Iqna ya habarto jami’an gwamnatin Syria na cewa, naurorin kakkabo makamai daga sama na kakkabo makaman makiya.

An kuma sami rahotannin fashewar wasu abubuwa a Iraki, (a Diyala da Salah Al-Din) kusa da Bagadaza babban birnin kasar.

A birnin Washington fadar gwamnatin Amurka ta White House ta ce babu hannun Amurka a cikin lamarin.

Wani mai magana da yawun fadar ya ce an sanar da mataimakiyar shugabar kasar Kamala Harris wadda ke yakin neman zabe a Texas halin da ake ciki.

bbc naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp