Isra’ila ta umarci dukkannin makarantu da ke arewacin ƙasar da su kulle har zuwa sai abin hali ya yi ya zuwa yammacin Litinin.
An kuma taƙaita taron jama’a a yankuna da dama na arewacin ƙasar da kuma wasu sassan yankin tsuburin Golan da Isra’ilar ta mamaye, inda ba a yarda mutum fiye da 10 su taru a waje sannan kuma an yarjewa mutum 100 haɗuwa a cikin gida.
Za kuma a rufe wuraren shaƙatawa
Ma’aikatar Lafiya ta Isra’ila ta ce an umarci asibitoci a arewacin Isra’ila da su yi ayyukansu a wurare masu tsaro.
Tuni dai asibitin Rambam da ke birnin Haifa ya koma ƙarƙashin ƙasa domin gudanar da ayyukansa.