Gwamnatin Isra’ila ta amince da tsawaita wa’adin tsagaita wuta a zirin Gaza na tsawon mako shida domin gudanar da azumin watan ramadan da kuma bikin Passover na Yahudawa.
A jiya Asabar ne matakin farko na tsagaita wutan ya ƙare.
Wakilin BBC ya ce Isra’ila na son a sako duka mutanen da aka yi garkuwa da su nan take ita kuma Hamas na son a ci gaba da mataki na biyu wanda ya ƙunshi tsagaita wuta na dindindin da kuma janyewar sojojin Isra’ila daga Gaza.
Hamas dai ba ta yi wani tsokaci kan shirin tsawaita tsagaita wutan na wucin gadi ba.