Ofishin ministan shari’ar Isra’ila wadda ta ta fayyace yadda za a hukumta wasu ƴan Isra’ila guda bakwai waɗanda suka fito daga Haifa da arewacin Isra’ilar da ake zargi da “yi wa ƙasar Iran aiki a lokacin yaƙin da ake yi da kafinsa.”
Sanarwar dai ta bayyana yadda aka biya mutanen “ɗaruruwan dubban dalolin Amurka ta hanyar kuɗin kirifto”.
Sanarwar ta ci gaba da cewa mutanen “sun ƙaddamar da ɗaruruwan ayyuka” inda suka ɗauki hotuna da kuma haɗa bayanan sirri da ya haɗa da kayan aikin rundunar IDF da wuraren da baturan tsarin tsaron Isra’ilar mai sulke suke.
Ana sa ran nan da wasu ƴan kwanaki ne za a fayyace laifukan da ake tuhumar mutanen.
Ofishin ya bayyana wannan al’amari da “ɗaya daga cikin manyan laifuka” a ƴan shekarun nan. In ji BBC.