Shugaban Amurka, Joe Biden ya yi wata kakkausar suka kan shugabancin Isra’ila inda ya alaƙanta rasa goyon bayan da ƙasar ta yi da abin da ya kira luguden wuta ba ji ba gani a Gaza.
Ya yi waɗan nan kalamai ne a wani taron kafa asusu da aka yi ranar Talata.
“Tsaron Isra’ila na iya jingina da Amurka amma a yanzu haka, tana da fiye da Amurka. Tana da Tarayyar Turai, tana da Turai, tana da galibin ƙasashen duniya,’ kamar yadda ya faɗa a Washington.
“Amma sun fara rasa goyon baya saboda hare-haren bom da ke faruwa,” in ji shi.