fidelitybank

Isra’ila ta nemi Rasha ta kare Yahudawa bayan al’umma sun fara far musu da duka

Date:

Isra’ila ta nemi Rasha ta kare “‘yan ƙasarta da kuma dukkan Yahudawa” bayan wani dandazon wasu mutane sun kutsa filin jirgin sama na Dagestan suna ta ihun ƙin jinin Yahudawa.

Wani bidiyo da aka wallafa a intanet ya nuna yadda mutanen cikin fushi suke shiga sassan filin jirgin da ke Makhachkala a Rasha suna neman matafiyan da suka sauka daga birnin Tel Aviv.

Wasu daga cikin mutanen sun shiga har kan titin tashin jirgin kuma suka zagaye shi.

Hukumar kula da sufurin jiragen sama ta Rasha, Rosaviatsia, ta ce ta shawo kan lamarin daga baya.

An rufe filin jirgin ranar Lahadi da dare. Rosaviatsia ta ce an sake buɗe shi a ranar Litinin, amma ta ce jiragen da suke zuwa daga Isra’ila “za a dinga sauya musu masauki zuwa wasu filayen jirgin na ɗan lokaci.”.

Kamfanin dillancin labarai na Rasha ya ce an kama mutum 60 daga cikin fusatattun mutanen yana mai ambato ma’aikatar harkokin cikin gida.

kano news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp