fidelitybank

Isra’ila ta lalata hanyoyin Hamas na ƙarƙashin ƙasa 130

Date:

Dakarun tsaron Isra’ila sun ce sun lalata hanyoyin ƙarƙashin ƙasa na Hamas 130 tun bayan fara kai farmakin ƙasa a Gaza.

A cikin wata sanarwa da dakarun Isra’ilar suka fitar sun ce “A halin yanzu dakarun yaƙin ƙasar suna aiki don fallasa tare da lalata kayayyakin ‘yan ta’adda na Hamas a Gaza, ciki har da hanyoyin ƙarƙashin ƙasa.”

“Ruwa da kuma ajiyar iskar oxygen da aka gano a cikin hanyoyin na nuni da shirye-shiryen Hamas na tsawaita zama a karkashin kasa.” in ji sanarwar.

A ranar Laraba ne rundunar sojin ta ce ta lalata wata hanyar ƙarƙashin ƙasa ta Hamas da ke kusa da wata makaranta da Hukumar Agaji ta Falasɗinu ke ɗaukar nauyinta a yankin Beit Hanoun da ke arewacin Gaza.

Rundunar ta kuma wallafa wani bidiyo da ake zargin ya nuna ɓarnar da aka yi a hanyoyin ƙarƙashin ƙasa da ke kusa da makarantar.

Isra’ila ta fara kai hare-hare a Gaza bayan harin Hamas a ranar 7 ga watan Oktoba, wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutum 1,400 tare da yin garkuwa da sama da 200.

Rundunar ta kuma tabbatar da mutuwar wani soja guda wanda ya kai adadin sojojin da aka kashe a harin ta ƙasa zuwa 31.

Ma’aikatar lafiya ta Hamas ta ce adadin mutanen da aka kashe a Gaza ya karu zuwa 10,569 tun lokacin da Isra’ila ta fara kai hare-haren ramuwar gayya.

legit nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Majalisar dokoki na son Iran ta yanke hulɗa da hukumar sanya ido kan makamashin nukiliya

Majalisar dokokin Iran ta kaɗa ƙuri’a domin yanke hulɗa...

Ƴan sanda sun kama mutum 26 da ake zargi da hannu a kashe-kashen Benue

Sufeto Janar na ‘ƴan sanda, Kayode Egbetokun, ya bayyana...

Ba dan mun yi wa Iran barna ba da har yanzu ba ta nemi sulhu ba – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya sake jaddada cewa harin...

Iran ta zartar da hukuncin kisa kan masu leken asiri

Kamfanin dillancin labarai na sashen shari'a a Iran ya...

Za mu ɗauki matakin hana sake faruwar kisan mutane – Gwamnatin Filato

Gwamnatin jihar Filato ta jaddada aniyarta ta ɗaukar mataki...

Babu barazanar tsaro a Abuja – Najeriya

Gwamnatin Tarayya ta ce, babu wata barazanar a babban...

Isra’ila za ta mayarwa da Iran martani duk da tsagaita wuta

Ministan tsaron Isra'ila, Katz ya bayyana cewa, ya ba...

Ba mu kai wa Isra’ila hari ba – Iran

Kafar watsa labarai ta Iran ta ruwaito gwamnatin ƙasar...

Duk da faduwar farashin mai NNPCL ya kara farashi

Kamfanin man fetur na Najeriya, NNPCL ya ƙara farashin...

Duk wasu ƙawayen Amurka za su ɗanɗanar kuɗarsu – Iran

Rundunar dakarun juyin juya halin Iran ta fitar da...

Iran ta mayar da martani kan sojojin Amurka dake Qatar

Kafofin yaɗa labaran Iran sun bayyana cewa ƙasar ta...

Faransa ba ta goyon bayan Amurka na kifer da gwamnatin Iran – Barrot

Ministan harkokin wajen Faransa ya ce, ƙasarsu ba ta...
X whatsapp