Dakarun tsaron Isra’ila sun ce sun lalata hanyoyin ƙarƙashin ƙasa na Hamas 130 tun bayan fara kai farmakin ƙasa a Gaza.
A cikin wata sanarwa da dakarun Isra’ilar suka fitar sun ce “A halin yanzu dakarun yaƙin ƙasar suna aiki don fallasa tare da lalata kayayyakin ‘yan ta’adda na Hamas a Gaza, ciki har da hanyoyin ƙarƙashin ƙasa.”
“Ruwa da kuma ajiyar iskar oxygen da aka gano a cikin hanyoyin na nuni da shirye-shiryen Hamas na tsawaita zama a karkashin kasa.” in ji sanarwar.
A ranar Laraba ne rundunar sojin ta ce ta lalata wata hanyar ƙarƙashin ƙasa ta Hamas da ke kusa da wata makaranta da Hukumar Agaji ta Falasɗinu ke ɗaukar nauyinta a yankin Beit Hanoun da ke arewacin Gaza.
Rundunar ta kuma wallafa wani bidiyo da ake zargin ya nuna ɓarnar da aka yi a hanyoyin ƙarƙashin ƙasa da ke kusa da makarantar.
Isra’ila ta fara kai hare-hare a Gaza bayan harin Hamas a ranar 7 ga watan Oktoba, wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutum 1,400 tare da yin garkuwa da sama da 200.
Rundunar ta kuma tabbatar da mutuwar wani soja guda wanda ya kai adadin sojojin da aka kashe a harin ta ƙasa zuwa 31.
Ma’aikatar lafiya ta Hamas ta ce adadin mutanen da aka kashe a Gaza ya karu zuwa 10,569 tun lokacin da Isra’ila ta fara kai hare-haren ramuwar gayya.