fidelitybank

Isra’ila ta kashe yara 2,360 a Falasɗinu – UNICEF

Date:

Asusun kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF, ya ce yara 2,360 ne suka mutu a hare-haren da Isra’ila ta kai a zirin Gaza a matsayin martani ga harin da Hamas ta kai a kudancin Isra’ila a ranar 7 ga watan Oktoba.

Kungiyar agajin, wacce ta yi magana game da “hare-haren da ba a saba gani ba”, ta ce yara 5,364 sun jikkata.

Tun bayan harin ba-zata da Hamas ta kai a ranar 7 ga watan Oktoba, sojojin Isra’ila ke kai hare-haren bama-bamai a zirin Gaza tare da shirya kai farmaki ta kasa a yankin da aka rufe.

“Halin da ake ciki a Zirin Gaza wani tabo ne a kan lamirinmu na gamayya. Adadin mace-mace da jikkatar yara na da ban mamaki,” in ji Adele Khodr, darektan UNICEF na yankin Gabas ta Tsakiya da Arewacin Afirka.

Ya ce yankin na Gaza na fama da matsalar karancin ruwan sha, tare da yin mummunar illa ga kananan yara wadanda ke da kashi 50 cikin 100 na al’ummar kasar.

UNICEF ta bukaci dukkan bangarorin da su amince da tsagaita bude wuta, samar da agajin jin kai da kuma sako duk wadanda aka yi garkuwa da su. (NAN)

spw

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp