Kungiyar Hamas ta yi ikirarin cewa an kashe ƴan Isra’ila 13 da wasu ‘yan kasashen waje da take garkuwa da su a Zirin Gaza a hare-hare ta sama da Isra’ila ta kai cikin sa’a 24,
Sanarwar da rundunar Izzedine al-Qassam ta fitar na cewa “an kashe fursunonin 13 ciki har da ‘yan kasashen waje a wurare guda biyar da jiragen yaƙin Isra’ila suka kai wa hari.”
Hamas ta kama tare da yin garkuwa da mutane kusan 150 a lokacin da ta kai harin ba-zata a ranar 7 ga Oktoba.
Ta yi barazanar kashe mutanen da take garkuwa da su, matukar Isra’ila ta jefa bama-bamai a gidajen fararen hula ba tare da gargadi ba.
Kamar yadda rahotanni suka shigo, Sakataren Tsaron Burtaniya Grant Shapps ya shaida wa ITV cewa zai so a yi taka-tsantsan kan wannan iƙirarin amma akwai “tsananin damuwa”.