fidelitybank

Isra’ila ta kashe mutane 500 a Lebanon

Date:

Ɗaruruwan ƴan Lebanon ne hare-haren Isra’ila ya kashe a cigaba da cigaba da luguden wuta da ƙasar ke yi da Lebanon.

Rahotanni na nuna an kashe kusan mutum 492, sannan an raunata sama da 1,645 a ƙasar Lebanon, kamar yadda Ma’aikatar Lafiyar ƙasar ta bayyana.

Wannan shi ne karon-batta mafi muni tsakanin Isra’ila da Hezbollah tun bayan da suka fara takun-saƙa a shekarar 2006′

Tuni dubban fararen hula suka tsere daga gidajensu domin tsira daga hare-haren a daidai lokacin da Isra’ila ta ce ta kai hari a wuraren Hezbollah guda 1,300.

Tun farko, Firaiministan Isra’ila, Benjamin Natanyahu ya yi kira ga fararen hula a Lebanon da su matsa daga wuraren da Isra’ilar take luguden wuta, sannan sojojin Isra’ila sun riƙa aika saƙonni ta wayar salula ga fararen hular suna nanata saƙon na Natanyahu.

Rahotanni a Lebanon sun nuna cewa Isra’ila na harin wani babban kwamandan Hezbollah mai suna Ali Karaki ne da ke Kudancin Lebanon, amma har yanzu babu tabbacin ko sun kashe shi, duk da cewa Hezbollah ta ce yana ƙalau.

Ita ma dai Hezbollah ta aika da sama da rokoki 200 a arewacin Isra’ila.

A ɗaya gefen kuma, Amurka ta ce za ta aika da ƙarin dakaru zuwa yankin Gabas ta Tsakiya.

Shugaban Amurka Joe Biden ya ce za su yi hakan ne domin hana ta’azzarar yaƙe-yaƙe domin mutane su koma gidajensu lafiya.

pulse news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp