Isra’ila ta ce ta kai hari a kusa da fadar shugaban ƙasar Syria da ke birnin Damascus don nuna goyon baya ga mabiya addinin Druz marasa rinjaye a kasar.
Firaminista Benjamin Netanyahu ya ce harin saƙo ne ga gwamnatin Syria kan kasarsa ba za ta zuba ido a aike dakarun sojin mabiya Sunni zuwa yankin da Druze suke ba.
Isra’ila ta kai harin ne a jiya Alhamis bayan arangamar da aka yi tsakanin mabiya addinin gargajiya na Drzue da ke kudancin birnin Damascs da dakarun gwamnati, inda gwamman mutane suka mutu.
A bangare guda kuma, shugaban mabiya addinin mai suna Sheikh Hikmat al-Hijri ya zargi gwamnatin Ahmad al-Sharaa da yi musu kisan ƙare-dangi.