Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi tsakanin Isra’ila da Iran, mazauna birnin Tehran sun ba da rahotannin jin ƙarar fashe-fashe a babban birnin da kuma birnin Karaj mai maƙwabtaka.
Kafofin yaɗa labaran Iran sun ce, sojojin Isra’ila ne suka kai hari kan cibiyoyin ƙera makami mai linzami da nukliyar Iran.
Rundunar sojin Isra’ila tun farko ta shawarci mutane a wata gunduma da ke Tehran da su fice daga gidajensu inda suka ce suna shirin kai hari.
Iran ta ce ta harba makamai masu linzami kan Isra’ila. Kawo yanzu babu rahoton rasa rai.