fidelitybank

Isra’ila ta gano gawargwaki uku na mutanen da aka yi garkuwa da su a Gaza

Date:

Dakarun sojin Isra’ila sun ce, sun gano gawar mutum uku da aka yi garkuwa da su a Zirin Gaza

A cewar rundunar sojin ƙasar ta IDF, mutanen su ne Shani Louk, da Amit Buskila, da Itzhak Gelerenter.

IDF ta ce an kashe su ne tun ranar 7 ga watan Oktoba kuma aka ɗauki gawar ta su zuwa Gaza.

Kafofin yaɗa labaran Isra’ila sun ruwaito cewa, an gano gawarwakin ne cikin wata hanyar ƙarƙashin ƙasa ta Hamas.

Mutane aƙalla 1,200 aka kashe lokacin da ‘yan gwagwarmyar Falasɗinawa suka aukawa Isra’ila ranar 7 ga watan Oktoba, sannan suka yi garkuwa da aƙalla mutane 252.

A matsayin martani, Isra’ila ta kashe sama da mutane 35,000, kamar yadda ma’ikatar lafiya ta Gaza ta tabbatar.

Sai dai Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, ya bayyana labarin da mai karya zuciya.

Ya na mai cewa, za su dawo da dukkan mutanen su da aka yi garkuwa da su, masu rai da matattu.

punch news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp