fidelitybank

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Date:

Tawagar masu aikin ceto a Isra’ila na ci gaba da neman mutanen da suka maƙale a ƙarƙashin ɓaraguzan gine-gine a birnin Tel Aviv.

An ji ƙarar fashewar manya-manyan abubuwa a wasu biranen Isra’ila ciki har da Tel Aviv da Jerusalem, yayin da Iran ta ci gaba da harba makamai masu linzami cikin dare zuwa Isra’ila.

Hotunan da aka wallafa a Intanet sun nuna yadda gine-gine suka ruguje.

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Isra’ila ta ce mutum biyar ne suka mutu sannan wasu sama da casa’in suka jikkata, a hare-haren na cikin dare.

Ƙasashen Isra’ila da Iran sun ci gaba da musayar wuta cikin dare a yayin da aka shiga kwana na huɗu a rikici tsakanin kashen biyu.

Hare-haren na Iran sun kuma shafin birnin Haifa da ke arewacin ƙasar, wanda ya kasance cibiyar babbar tashar jirgin ruwa da matatar matar mai.

Tun da farko Iran ta tabbatar da cewa an kashe shugaban sashen leƙen asiri na rundunar dakarun ƙare juyin juya hali ta ƙasar da mataimakinsa da wani kwamanda a wani harin da Isra’ila ta kai birnin Tehran.

Ma’aikatar lafiyar Iran ta ce aƙalla mutum 224 ne suka mutu tun bayan aka fara kai mata hare-haren.

A nata ɓangare Isra’ila ta ce kawo yanzu an kashe mutum 19, tun bayan fara hare-haren

vanguardnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Izak ya na ɗaukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa ƴan Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa ƴanbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen ƙauyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...

Ba za mu jingine yajin aiki ba har sai an biya mana buƙatun mu – Ma’aikatan Jinya

Shugaban ƙungiyar ma'aikatan jinya ta Najeriya, Morakinyo-Olajide Rilwan ya...

Za a fara yi wa Dalibai gwajin kwaya kafin su shiga jami’a – NDLEA

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta fara yi wa...

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...
X whatsapp