fidelitybank

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Date:

Tawagar masu aikin ceto a Isra’ila na ci gaba da neman mutanen da suka maƙale a ƙarƙashin ɓaraguzan gine-gine a birnin Tel Aviv.

An ji ƙarar fashewar manya-manyan abubuwa a wasu biranen Isra’ila ciki har da Tel Aviv da Jerusalem, yayin da Iran ta ci gaba da harba makamai masu linzami cikin dare zuwa Isra’ila.

Hotunan da aka wallafa a Intanet sun nuna yadda gine-gine suka ruguje.

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Isra’ila ta ce mutum biyar ne suka mutu sannan wasu sama da casa’in suka jikkata, a hare-haren na cikin dare.

Ƙasashen Isra’ila da Iran sun ci gaba da musayar wuta cikin dare a yayin da aka shiga kwana na huɗu a rikici tsakanin kashen biyu.

Hare-haren na Iran sun kuma shafin birnin Haifa da ke arewacin ƙasar, wanda ya kasance cibiyar babbar tashar jirgin ruwa da matatar matar mai.

Tun da farko Iran ta tabbatar da cewa an kashe shugaban sashen leƙen asiri na rundunar dakarun ƙare juyin juya hali ta ƙasar da mataimakinsa da wani kwamanda a wani harin da Isra’ila ta kai birnin Tehran.

Ma’aikatar lafiyar Iran ta ce aƙalla mutum 224 ne suka mutu tun bayan aka fara kai mata hare-haren.

A nata ɓangare Isra’ila ta ce kawo yanzu an kashe mutum 19, tun bayan fara hare-haren

jalingo news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp