fidelitybank

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Date:

Tawagar masu aikin ceto a Isra’ila na ci gaba da neman mutanen da suka maƙale a ƙarƙashin ɓaraguzan gine-gine a birnin Tel Aviv.

An ji ƙarar fashewar manya-manyan abubuwa a wasu biranen Isra’ila ciki har da Tel Aviv da Jerusalem, yayin da Iran ta ci gaba da harba makamai masu linzami cikin dare zuwa Isra’ila.

Hotunan da aka wallafa a Intanet sun nuna yadda gine-gine suka ruguje.

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Isra’ila ta ce mutum biyar ne suka mutu sannan wasu sama da casa’in suka jikkata, a hare-haren na cikin dare.

Ƙasashen Isra’ila da Iran sun ci gaba da musayar wuta cikin dare a yayin da aka shiga kwana na huɗu a rikici tsakanin kashen biyu.

Hare-haren na Iran sun kuma shafin birnin Haifa da ke arewacin ƙasar, wanda ya kasance cibiyar babbar tashar jirgin ruwa da matatar matar mai.

Tun da farko Iran ta tabbatar da cewa an kashe shugaban sashen leƙen asiri na rundunar dakarun ƙare juyin juya hali ta ƙasar da mataimakinsa da wani kwamanda a wani harin da Isra’ila ta kai birnin Tehran.

Ma’aikatar lafiyar Iran ta ce aƙalla mutum 224 ne suka mutu tun bayan aka fara kai mata hare-haren.

A nata ɓangare Isra’ila ta ce kawo yanzu an kashe mutum 19, tun bayan fara hare-haren

benue news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...
X whatsapp