Ofishin Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, ya ce matakin mayar da martani kan harin da Iran ta kai makonni biyu da suka gabata zai dogara ne kan buƙatun tsaron Isra’ila.
Sanarwar da aka fitar a daren jiya ta kasance martani ne ga wani rahoto da jaridar Washington Post ta wallafa wanda ya ce Mr Netanyahu ya shaida wa shugaba Biden cewa ba zai kai hari kan tashoshin Nukiliyar Iran ba.
Rahoton ya ce Isra’ila za ta takaita martanin na ta domin kaucewa yin tasiri kan zaɓen Amurka da za a yi a watan mai zuwa.