Rundunar sojin Isra’ila ta ce cikin gawar da Hamas ta ba su jiya a Gaza a matsayin na Shiri Bibas, ba ita ba ce.
Haka kuma sun ce ƙananan yaranta biyu da aka dawo da gawarwakinsu, kisan gilla aka yi musu.
Sojojin Isra’ila ta zargi Hamas da karya yarjejeniyar tsagaita wuta da buƙatar ta dawo musu da gawar Shiri Bibas.
A jiya Alhamis ne Hamas ta miƙa gawarwakin mutum huɗu, inda ta ce daga ciki akwai gawar Shiri da ƴaƴanta biyu, inda Isra’ila ta fara binciken ƙwaƙwaf domin tantance gawarwakin.