Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce Isra’ila ta kaɗa gangar yaki, kuma ƙasarsa za ta ci gaba da mayar da mummunan martani kan hare-haren da ake kai ma ta.
Ya ce “bai kamata su yi tunanin cewa za su kaddamar da hare-hare kuma shikenan ba, su ne suka fara, su ne suka kunna wutar yaƙi kuma ba za mu bari su tafi haka nan ba.
A wani taron gaggawa na kwamitin tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya, jakadan Iran ya ce hare-haren da Isra’ila ta kai ya yi sanadin mutuwar mutum 78 – akasarinsu fararen hula – tare da jikkata wasu da dama.
An kaddamar da hare-haren ne kan cibiyoyin nukiliya da na soji, amma sun shafi fararen hula da dama.
Isra’ila ta ce ta kai farmakin ne domin hana Iran mallakar makamin nukiliya.