fidelitybank

Isra’ila ta aikata laifin yaƙi bisa harin da ta kai sansanin Jabalia a Falasɗinu – MDD

Date:

Ofishin kare haƙƙi na MDD ya wallafa saƙo a dandalin X, wanda aka sani da Twitter a baya, game da harin Isra’ila kan sansanin ‘yan gudun hijira na Jabalia ranar Talata.

“Ganin yawan fararen hular da aka kashe da kuma girman ɓarnar da aka yi a sansanin Jabalia, muna da damuwa babba cewa wannan hari ne kan mai tsautsayi da zai iya zama laifin yaƙi,” a cewar hukumar kare haƙƙi ta MDD.

A jiya ne jiragen yaƙin Isra’ila suka kai munanan hare-hare kan sansanin da yamma.

Hotunan da aka ɗauka sun nuna mummunar ɓarnar da aka yi, inda bama-bamai suka haƙa ramuka kuma ɓaraguzai da ƙarafa suka zagaye wurin baki ɗaya.

Kusan mutum 100 aka kashe a harin, ciki har da ƙananan yara.

Isra’ila na cewa ta kashe wani babban kwamandan Hamas a sansanin tare da lalata hanyar ƙarƙashin ƙasa da ƙungiyar ke amfani da ita.

Ta kuma ce tana bincike kan rahotonnin “ɓarna da kuma kisan fararen hula da aka yi”.

www.nigerianews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp