Isra’ila ta ce ta kama mambobin ƙungiyar jihadi ta Falasɗinawa a yankin da ta mamaye na Gaɓar Yamma da Kogin Jordan ko kuma West Bank bayan hare-haren da ta kai a Birnin Gaza.
Mutum aƙalla 11 ta kashe a hare-haren ta sama, ciki har da yarinya mai shekara biyar da kuma jagoran gwagwarmaya na ƙungiyar ta Palestinian Islamic Jihad (PIJ), Tayseer Jabari.
Tashin hankalin na baya-bayan nan shi ne mafi muni tsakanin Isra’ila da Falasɗinawa cikin shekara ɗaya da ‘yan watanni.
Yaƙin da aka yi na kwana 11 a watan Mayun 2021 ya jawo kisan Falasɗinawa fiye da 200 da kuma ‘yan Isra’ila kusan 12 kafin a tsagaita wuta.
Su ma Falasɗinawa sun mayar da martani da harba makaman roka fiye da 100 cikin Isra’ila a ranar Juma’a. A cewar BBC.