fidelitybank

Isra’ila sai ta ɗanɗana kuɗar ta – Iran

Date:

Iran ta yi alƙawarin mayar da martani ga abin da ta kira harin Isra’ila wanda ya lalata ofishin jakadancinsa da ke Damascus babban birnin Syria.

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce Isra’ila za ta yi da na sanin kai harin, yayin da shugaba Ebrahim Raisi ya dage cewa dole za a ɗauki mataki.

Gidan talabijin na Iran ya ruwaito mutuwar dakarun juyin juya-hali bakwai har da janar-janar biyu da ƴan Syriya shida.

Rundunar sojin Isra’ila ta ce ba ta yi magana kan rahotannin da kafafen yaɗa labarai suka ruwaito ba.

Sai dai wani babban jami’in gwamnatin Isra’ila ya faɗa wa Reuters cewa waɗanda aka kashe na da hannu a hare-hare da dama da aka kai kan gine-ginen Isra’ila da Amurka kuma suna da ƙudirin kai ƙarin hare-hare.

Sun kuma bayyana cewa ba ofishin jakadancin aka nufa da harin ba. In ji BBC.

Jaridar New York Times ta ruwaito jami’an Isra’ila huɗu suna tabbatar da cewa Isra’ila ta kai harin tare da musanta cewa ginin ofishin jakadanci ne.

Isra’ila ta tabbatar da kai ɗaruruwan hare-hare a shekarun baya-bayan nan kan cibiyoyi a Syriya da ta ce suna da alaƙa da Iran da ƙungiyoyin mayaƙa da suke samun tallafin dakarun juyin-juya hali.

nan news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp